Wani dan sanda da yayi tatul da giya ya kashe waɗansu matasa biyu a wajen murnan shigowar sabuwar shekara, lamarin ya faru ne a Kings square dake Birnin Benin ta Jahar Edo. Shidai jami'in tsaron yazo halba bindiga a sama ne domin murnan shigowar shekarar 2019 amman ya kuskure juya bindigan zuwa sama inda ya samu waɗansu matasa dake wurin ya bindige su, anan take daya daga cikin matasan ya sheka lahira, dayan matashin kuma ya cika ne bayan da aka gaza samun jami'an kula da lafiya da zasu iya bashi taimakon gaggawa.
Dan takaran shugaban kasa a jam’iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar ya fitar da dubarun da zai dauka domin ganin kawo karshen matsalar tsaro a jahar Zamfara. A cikin sakon hoton video daya fitar a shafinsa na twitter yace, “Alummar Jahar Zamfara ina tare daku a cikin wannan yanayin da kuka tsinci kanku a hannun mahara wadanda suke sace dukiyar ku kuma suke kashe maku al’umma tare da barnatar maku da dukiyoyin ku” Zuciya na tana kadawa sosai akan yanayin da kuka tsinci kanku in addua’an Allah ya kawo maku karshen wannan kashe-kashe da kuma irin wahalar da kuke ciki” "Ni dan takaran shugabancin Kasar nan ne, ina mai tabbatar ma al’ummar jahar Zamfara cewan idan har kuka zabe ni a matsayin shugaban Kasa a ranan 16 ga watan February 2019 bazan zarce wata daya ba da shan rantsuwan kama aiki ba zan turo rundunar zaratan jami’an tsaron na sojoji da yan sanda dubu talatin (30.000) domin su fatattaki wadannan yan ta’adan da suke kashe al’umma a Jahar taku." "A lokacin zaben ...
SIYASAR MU A YAU Godiya ta tabbata ga Allah Subahanhu wata'ala daya bani ikon yin tsokachi ko ince fadakarwa a bisa abubuwan da suke faruwa ga SIYSAR MU A YAU. musamman a wannan lokichin da zabe ke kara karatowa a kasarsamu. Da farko abinda muka fahimta da siyasa shine, kusantar al'umma zuwa ga gwamnati, sannan gwamnati ta san mene matsalar al'ummarta, ta hanyar bamu damar mu zabi mutanen da muke tsammanin sune adilai a tare da mu, domin su shugabanche mu. to amman KASH!!! Shin wai jamma'a muna-nufin har yanzu bamu fahimchi ko mai-nene SIYASA BA? shin jama'a har yanzu bamu san adilin daya dace ya jagoranche mu bane? to ko son zuciya ne da rashin sanin ciwon kai ne ke damun mu? ya kamata mu chire kwadayi a tare da mu, mu farka daga magagin bracin da muke yi domin musan matsalolin da suke addabarmu. mu kore azzaluman shugabanni daga mulki, mu kori 'yan baradan su da azzaluman da ke goya masu baya, kai da ma duk wani wanda bai kaunan kawo cigaba a kasa...
Comments
Post a Comment