Posts

Showing posts from June, 2013

AMERICA DA BOKO HARAM

BOSTON, MA — Babban kwamandan Rundunar Sojojin Amurka a Afirka, Janar David Rodriguez, yace sojojin Amurka su na sanya idanu sosai a kan take-taken ‘yan Boko Haram na Arewacin Najeriya, a yayin da kungiyar take fadada huldarta da wasu kungiyoyin ta’addanci dake nahiyar Afirka. Janar Rodriguez, wanda ya karbi ragamar shugabancin wannan runduna da ake kira AFRICOM a takaice, wadda kuma ta ke da hedkwata a Stuttgart dake kasar Jamus, yace daya daga cikin babban abinda suka bayar da muhimmanci gare shi, shi ne yaduwar kungiyoyin tsagera a Afirka. Yace musamman ma, sun sanya idanu a saboda damuwa da suke da ita ta musamman kan kungiyar Boko Haram a saboda a wani bangare, kungiyar tana ci gaba da fadada huldarta da kungiyoyin ta’addanci na yankin. Ya ce, “mun damu da wannan domin irin wannan hulda tana fadada dama da fadada kwarewa ga irin wadannan kungiyoyi, kuma mun san Boko Haram kungiya ce mai son zub da jini sosai. Kungiya ce da ta ke yin illa ga yankin arewacin Najeri

Matasan Arewa

Shin a matsayenka na matanshe na area wace kungiyace kake cikinta domin ganin ka bayar da taka gudun muwa wajen cigaban arewa? Ina kira ga matasanmu na arewa da mu kirkiri kungiyayo na taimakon kai-da-kai domin ma samu hanyar da zamu furta ma duniya abun dake cikin ranmu game da irin canjin da mukeso ma kawo ma yankin mu da kuma kasar mu ga baki daya. Ina kira ga manyan arewa da su tuna da cewan haqin tallafa ma matasanmu ya rataya a wuyansu na manya, mu kuma matasa haqqin tashi da kuma zage damtse wajen kawo cigaba a yankinmu ya rataya a wuynamu, idan mukayi dubi da kasashen da suka cigaba kungiyoyi suna da matkur tasiri ga yan kasan da kuma kawo masu cigaba ta ko wane irin fanni.