Posts

Showing posts from 2014

TAYA MURNA GA ALHAJI ABUBAKAR SANI BELLO (ABU LOLO)

A madadina da iyalan gidan Alhaji Sale Kaboji, Mai-dakina, Nana Firdausi da kuma yarona Yasir, Muna taya daukacin al'ummar jahar Naija musamman 'yayan jami'yyar APC Murnan lashe zaben fidda gwani da jam'iyyar da gabatar a jiya Alhamis, Inda Alhaji Abubakar San Bello (Abu Lolo) ya lashe zaben, a matsayin wanda zaiyi ma jam'iyyar takara a babban zabe mai zuwa na 2015, Muna tayashi murna da kuma fatan alheri ga jahar mu ta Naija, dama daukacin kasar mu Nigeria baki daya. Ubangiji Allah ya bashi nasara a babban zabe mai zuwa. Ameen

Demokradiyya a kasashen mu na Afrika

Shin dama haka demkorad'iyyar take a sauran kasashen duniya? Kodai a kasashen Afrika ne lamarin yake a haka? Akasarin talakawan 'kasar nan bamu san ko mai nene romon demokra'diyya ba, 'yan tsirarun mutane ne kawai suke chin wannan romon ma Demokradiyya a kasashen mu na Afrika. Idan mukayi duba ga kasar Libya wacce take cikin wani mawuyacin hali a wannan lokacin sanadiyyar Demokradiyyar da kasashen yamma suke ikirarin itace hanya mai cike da walwala da kuma 'yanci, zamu ga wannan Demokradiyyar ta wurga kasar ta Libya cikin wani matsananci hali batare da samun romon da kasashen yamma suke cewa akwai a ciki ba. Tsohon Shugaban Kasar Libyar Muammar Gaddafi yayi ma dukkan daukacin al'ummar kasar abubuwan da suke sunma wuce da akira su da demokradiyya muddun kishin kasa ne da kuma cigaban kasa al'umma ke bukta' amman idan walwala ne ta 'yan tsiraru daga kasashen yamma da kuma bada dama ga 'yan kasa suyi zabe, lallai a wanchan lokacin kasar Libya

INNALILLAHI WANNI-ILAHIR RAJI’UN!

Misalin karfe 7:37 na yamma ne 13/6/2014 ranar juma’a ina zaune ni kadai, sai ga kiran waya daga wata bakuwar number ta Airtel, ashe wannan kiran daga daya daga cikin abokanaina ne ya kira ni domin shaida mani rasuwar abokinmu Husaini Aliyu Nakofa. INNALILLAHI WANNI-ILAHIR RAJI’UN! Lallai nayi babban rashi aboki na rasuwa Husaini Aliyu Nakofa, abokin zama ne kuma ‘dan uwa na kwarai mai kula da addini, sannan ga hakuri da sanin girman mutane tare dashi, mutum ne mai son zumunci tare da ziyaran abokanai kowane lokaci, akwai natsuwa da kuma iya zama cikin mutane. Hussaini Aliyu Nakofa mutum ne mai kula da addini, baya wasa da lamarin daya shafi addini musamman ma salah, A duk lokacin da Husaini Aliyu ya rasa Sallah Asuba cikin jam’I, idan muka fito wurin aiki yakan nuna mani damuwarsa sosai kan rashin samun sallah asuba cikin jam’I da baiyi ba, Hussaini Aliyu Nakofa mutum ne mai kokarin yin azumi na nafila tare da kokarin ganin ya faranta ma mahaifiyarsa rai kowane lokaci. Kowane lo

Masarautar Kano

Da fatan mun wayi gari cikin koshin lafia Marasa lafia daga cikinmu Muna rokon Allah ya basu lafia, mu kuma da mukeda lafiar mun rokon A;;ah ya kara muna lafiyar. Duk dayake Allah bai bani iko nayi rubutu akan abubwan da suke faruwa a masarautar Kano ta nadi sabon sarki mai martaba malam Sanusi Lamido Sanusi ba, cikin ikon Allah yau na samu daman da zan danyi tsokaci akan jita-jitar da jama’a ke yadawa a cikin garin Kano da kuma yawancin shafukan sada zumunta musamman ma na facebook. Kamar yadda muka sani ne cewan a al’adance babu rowan shugaban kasa kan lamarin daya shafi nadin sabon sarki a kowace masarauta kowa, barre har shi shugaban kasar ya samu daman tsige sarkin ko wani basarake kokuma yayi masa wata barazana, duk dayake akwai rawar da gwamnoni suke takawa wajen nada sabon sarki da kuma tafiyar da wadansu harkoki na fada. Ya kamata jama’a mu san cewan shugaban kasa bashida hurumin dakatar da koda sakamakon zabe ne da hukumar zabe ta rigaya ta fitar barre kuma dakatar da

Rashin Adalcin Duniya (2)

Rashin Adalcin Duniya (2) Idan mukayi duba akan lamarin satar yara 'yan makaranta da kungiyar Boko Haram ta sace su kusan 200 da 'yankai, inda hankali duniya ya karkata kan gwamnatin Nigeria domin ganin an ceeto wadannan yaran, inda har gwamnatin kasar mu Nigeria tayi tayin neman taimako daga manyan kasashen duniya kan ceto wadannan yaran 'yan makaranta. Duk dayake lamarin daya shafi tsaro lamari ne dake bukatan taka tsan-tsan da kuma boye wadansu surruka tare da amfani da kwararun jami'ai. Toh babban abundake daure mani kai shine yadda gangamin kungiyoyi ke fuskanta barazana a nan cikin gida Nigeria tare kuma da lafawar yawan gangamin da kungiyoyi ke shiryawa kan gwamnati takara matsa kaimi wajen ceto wadannan yaran. Kungiyar #BringBackOurGirls ta fuskanci barazana da wata kungiyar mai suna irin nata a Unity fourtune Abuja, wurin da suke taruwa domin isar ma gwamnati da sakon su, Inda lamarin ke daure mani kai akan ceewan su wadannan kungiyoyi idan har don Alla

Rashin Adalcin Duniya (1)

Rashin Adalcin Duniya (1) Zan soma wannan rubutun mai taken Rashin Adalcin Duniya akan kasarmu Nigeria, musamman lamarin tsaro daya tabar-bare a yankin arewacin kasar nan. A ko'ina a duniya jama'a sun san da sanin cewan babu wani aiki da zai iyaa gagaran gwamnati, gwamnati kowace kasa kuwa a duniya, idan kuma har wannan aikin ya gagari gwamnati toh dole ne ta tashi ta nemo taimako daga wajen sauran takwarorinta na duniya dommin dakile matsalar datake fuskanta, ganin haka yasa muke ganin babu wani aiki da zai gagare gwamnati kasancewar idan gwamnati daya ta kasa toh akwai masu iya tallafa mata daga wadansu kasashe. Toh amman kafin gwamnati tace ta kasa har takai ga nemo taimako daga wajen sauran takwarorin ta na duniya toh dole ne sai 'yan kasa sun yaba tare kuma da ganin iyakacin kokarin da gwamnati tayi. A kasar mu Nigeria jama'a da yawa basu gani ba balle kuma su yaba ma gwamnati kasar tamu ba akan ikirarin datakeyi na yaki da kungiyar ta'addincin nan wato Bo
#BringBackOurGirls Tun lokacin da aka sace yara nan 'yan makaranta banji wani bayani tsayaye daga bakin jam'ian tsaro ba ko kuma daga fadar shugaban kasa ba. Iyakaci kawai iyaye yaran ne kawai ke naso kokarin ganin sun samu bayanai da kansu, duk da irin matsa kaimi dda jama'a da kuma kungiyoyi keyi a kasar nan dama duniya baki daya. A karshe dai munji cewan jami'an tsaro na kasar America zasu kawowa Nigeria dauki domin ganin an gano su wadannan yaran da aka sace. Toh ni abubwa dake daure mani kai sannan nake ganinsu da alamun tambaya sune: Shin sauran yaran nan da suka samu tserewa daga hannun 'yan kungiyar ta Boko Haram basuyi magana da wata kafar yada labari bane? Domin nidai banji wata hira da akayi da daya daga cikin yaran da aka sacen suka samu daman kubuta ba. Sannan a duk inda ake bincike abunda ya bace akan bi sawun wata alamu da aka gani imma sawun inda abunda ya bace yabi kokuma wane bayani da aka samu gamsashe, Toh shin wadannan yaran da Allah yasa s

Nigeria!

Nigeria Lamarin kungiyar ta'addancin da ake kira da Boko Haram tana kawo cikas sosai a lamarin cigaban yankinmu na arewa, sannan kungiyar ta sanya ma yawancin 'yan arewacin kasar nan muslmai zargi a zukatansu kan yadda kungiyar take kashe mutane ba tare da wani haqqi ba da sunan kungiyar addini. Da dama jama'an arewa sunayi ma kungiyar Boko Haram kallo ta fuskoki da dama. Wasu nayima kungiyar kallon cewan kungiyar kiristoci ce ta Nigeria ke tafiar da kungiyar domin rage yawan muslman kasar nan. Wasu kuma nayi mata kallon 'yan siyasa ne ke tafiyar da kungiyar donmin ganin sun cimma burinsu akan zabe mai zuwa na 2015. Wadanda ke cikin gwamanti da kuma 'yan adawa kowa na daura ma juna laifi akan hare-haren da kungiyar ke kawai da kuma cewan suna daya daga cikin masu tallafawa kungiyar. Kiristoci dake a gefe kuma sunayi mata kallon kungiya ce ta addini, inda wadansu muslmai masu zafafen ra'ayi suka kafata domin yawa ragen kiristocin dake yankin. A gefe daya k

Fashin Bakin Jawabin Shugaban Kasa

A ciki ‘yan kwanankin nan 'yan Nigeria muna ta daga murya da nuna rashin yardar mu akan bacewar kudi 20B$ daga assusun ma'aikatar man fetur na kasa da kuma nuna rashin yarda akan yara 'yan makaranta masu rubuta jarabawar karshe na secondary da aka sace a garin Chibok na jahar Borno, sai gaya a cikin hirar da shugaban kasa Jonthan yayi da 'yan jaridu a jiya yana cewan "Ban san inda wadannan yaran suke ba, sannan maganar kudi da ake cewan sun bace ban sani ba" Wato ya kasance kenan duk tayar da jijyan wuyoyin da talakawa, iyaye da kuma masu fashin baki suka dingayi a kasar nan ya zamo na Banza kenan, domin kuwa wanda yake shugabantar kasar kuma wanda ya dace ya kasance a sahu na gaba-gaba wajen nemo ma talakwa haqqinsu a kasar nan yayi wannan maganar. Shin a haka zamu cigaba da kasanncewa a tare da irin wannan shugaban wanda bai san nauyin day a rataya a wuyansa ba? A duk inda shugaba ya kasance ana son ya kasance ne wanda dukkanin muhimman abubawan na tafiya