#BringBackOurGirls
Tun lokacin da aka sace yara nan 'yan makaranta banji wani bayani tsayaye daga bakin jam'ian tsaro ba ko kuma daga fadar shugaban kasa ba.
Iyakaci kawai iyaye yaran ne kawai ke naso kokarin ganin sun samu bayanai da kansu, duk da irin matsa kaimi dda jama'a da kuma kungiyoyi keyi a kasar nan dama duniya baki daya.
A karshe dai munji cewan jami'an tsaro na kasar America zasu kawowa Nigeria dauki domin ganin an gano su wadannan yaran da aka sace.
Toh ni abubwa dake daure mani kai sannan nake ganinsu da alamun tambaya sune:
Shin sauran yaran nan da suka samu tserewa daga hannun 'yan kungiyar ta Boko Haram basuyi magana da wata kafar yada labari bane? Domin nidai banji wata hira da akayi da daya daga cikin yaran da aka sacen suka samu daman kubuta ba.
Sannan a duk inda ake bincike abunda ya bace akan bi sawun wata alamu da aka gani imma sawun inda abunda ya bace yabi kokuma wane bayani da aka samu gamsashe, Toh shin wadannan yaran da Allah yasa suka kubuta basu samu daman baiwa jami'an tsaro bayanai banee game da inda aka nufa dasu ba da kuma wadansu bayanai masu alaka da sansanin 'yan kungiyar Boko Haram ba?
Shin ta wane bangare ne jami'an tsaron mu suka kasa?
Rashin kayan aiki ne kokuma rashin kwarewa ne?
Mai nene makomar manyan jami'ian tsaron namu dasuka kasa? Da kuma dumbin dukiyar da ake ware masu?
Ya kamata mu samu cikakken bayani akan wannan lamarin ba wai a dinga yi muna jawabi a dunkule ba.
Jawabi mai ma'ana kamar yadda yake faruwa a kasar Malysia na bacewar jirgin sama.
Zan Kawo Karshen Kashe-Kashen Zamfara Cikin Wata Daya - ATIKU ABUBAKAR
Dan takaran shugaban kasa a jam’iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar ya fitar da dubarun da zai dauka domin ganin kawo karshen matsalar tsaro a jahar Zamfara. A cikin sakon hoton video daya fitar a shafinsa na twitter yace, “Alummar Jahar Zamfara ina tare daku a cikin wannan yanayin da kuka tsinci kanku a hannun mahara wadanda suke sace dukiyar ku kuma suke kashe maku al’umma tare da barnatar maku da dukiyoyin ku” Zuciya na tana kadawa sosai akan yanayin da kuka tsinci kanku in addua’an Allah ya kawo maku karshen wannan kashe-kashe da kuma irin wahalar da kuke ciki” "Ni dan takaran shugabancin Kasar nan ne, ina mai tabbatar ma al’ummar jahar Zamfara cewan idan har kuka zabe ni a matsayin shugaban Kasa a ranan 16 ga watan February 2019 bazan zarce wata daya ba da shan rantsuwan kama aiki ba zan turo rundunar zaratan jami’an tsaron na sojoji da yan sanda dubu talatin (30.000) domin su fatattaki wadannan yan ta’adan da suke kashe al’umma a Jahar taku." "A lokacin zaben ...
Comments
Post a Comment