#BringBackOurGirls
Tun lokacin da aka sace yara nan 'yan makaranta banji wani bayani tsayaye daga bakin jam'ian tsaro ba ko kuma daga fadar shugaban kasa ba.
Iyakaci kawai iyaye yaran ne kawai ke naso kokarin ganin sun samu bayanai da kansu, duk da irin matsa kaimi dda jama'a da kuma kungiyoyi keyi a kasar nan dama duniya baki daya.
A karshe dai munji cewan jami'an tsaro na kasar America zasu kawowa Nigeria dauki domin ganin an gano su wadannan yaran da aka sace.
Toh ni abubwa dake daure mani kai sannan nake ganinsu da alamun tambaya sune:
Shin sauran yaran nan da suka samu tserewa daga hannun 'yan kungiyar ta Boko Haram basuyi magana da wata kafar yada labari bane? Domin nidai banji wata hira da akayi da daya daga cikin yaran da aka sacen suka samu daman kubuta ba.
Sannan a duk inda ake bincike abunda ya bace akan bi sawun wata alamu da aka gani imma sawun inda abunda ya bace yabi kokuma wane bayani da aka samu gamsashe, Toh shin wadannan yaran da Allah yasa suka kubuta basu samu daman baiwa jami'an tsaro bayanai banee game da inda aka nufa dasu ba da kuma wadansu bayanai masu alaka da sansanin 'yan kungiyar Boko Haram ba?
Shin ta wane bangare ne jami'an tsaron mu suka kasa?
Rashin kayan aiki ne kokuma rashin kwarewa ne?
Mai nene makomar manyan jami'ian tsaron namu dasuka kasa? Da kuma dumbin dukiyar da ake ware masu?
Ya kamata mu samu cikakken bayani akan wannan lamarin ba wai a dinga yi muna jawabi a dunkule ba.
Jawabi mai ma'ana kamar yadda yake faruwa a kasar Malysia na bacewar jirgin sama.
Dan Sanda Ya Kashe Matasa Biyu A Benin
Wani dan sanda da yayi tatul da giya ya kashe waɗansu matasa biyu a wajen murnan shigowar sabuwar shekara, lamarin ya faru ne a Kings square dake Birnin Benin ta Jahar Edo. Shidai jami'in tsaron yazo halba bindiga a sama ne domin murnan shigowar shekarar 2019 amman ya kuskure juya bindigan zuwa sama inda ya samu waɗansu matasa dake wurin ya bindige su, anan take daya daga cikin matasan ya sheka lahira, dayan matashin kuma ya cika ne bayan da aka gaza samun jami'an kula da lafiya da zasu iya bashi taimakon gaggawa.
Comments
Post a Comment