Posts

Showing posts from June, 2014

INNALILLAHI WANNI-ILAHIR RAJI’UN!

Misalin karfe 7:37 na yamma ne 13/6/2014 ranar juma’a ina zaune ni kadai, sai ga kiran waya daga wata bakuwar number ta Airtel, ashe wannan kiran daga daya daga cikin abokanaina ne ya kira ni domin shaida mani rasuwar abokinmu Husaini Aliyu Nakofa. INNALILLAHI WANNI-ILAHIR RAJI’UN! Lallai nayi babban rashi aboki na rasuwa Husaini Aliyu Nakofa, abokin zama ne kuma ‘dan uwa na kwarai mai kula da addini, sannan ga hakuri da sanin girman mutane tare dashi, mutum ne mai son zumunci tare da ziyaran abokanai kowane lokaci, akwai natsuwa da kuma iya zama cikin mutane. Hussaini Aliyu Nakofa mutum ne mai kula da addini, baya wasa da lamarin daya shafi addini musamman ma salah, A duk lokacin da Husaini Aliyu ya rasa Sallah Asuba cikin jam’I, idan muka fito wurin aiki yakan nuna mani damuwarsa sosai kan rashin samun sallah asuba cikin jam’I da baiyi ba, Hussaini Aliyu Nakofa mutum ne mai kokarin yin azumi na nafila tare da kokarin ganin ya faranta ma mahaifiyarsa rai kowane lokaci. Kowane lo

Masarautar Kano

Da fatan mun wayi gari cikin koshin lafia Marasa lafia daga cikinmu Muna rokon Allah ya basu lafia, mu kuma da mukeda lafiar mun rokon A;;ah ya kara muna lafiyar. Duk dayake Allah bai bani iko nayi rubutu akan abubwan da suke faruwa a masarautar Kano ta nadi sabon sarki mai martaba malam Sanusi Lamido Sanusi ba, cikin ikon Allah yau na samu daman da zan danyi tsokaci akan jita-jitar da jama’a ke yadawa a cikin garin Kano da kuma yawancin shafukan sada zumunta musamman ma na facebook. Kamar yadda muka sani ne cewan a al’adance babu rowan shugaban kasa kan lamarin daya shafi nadin sabon sarki a kowace masarauta kowa, barre har shi shugaban kasar ya samu daman tsige sarkin ko wani basarake kokuma yayi masa wata barazana, duk dayake akwai rawar da gwamnoni suke takawa wajen nada sabon sarki da kuma tafiyar da wadansu harkoki na fada. Ya kamata jama’a mu san cewan shugaban kasa bashida hurumin dakatar da koda sakamakon zabe ne da hukumar zabe ta rigaya ta fitar barre kuma dakatar da