Gwamnatin Tarayya Zatayi Zama Da Kungiyoyin NLC Da Kuma ASUU A Yau

A yau Litinin ne shugabannin kungiyar ƙwadago na
Nigeria (NLC) zasuyi zama da gwamnatin tarayya domin samar da mafitar karshe akan yajin aikin da suke shirin zuwa wanda ya shafi mafi karanci albashin ma'aikata, ministan ƙwadago da kuma ministan kasafi da tsare-tsare game da ministan kudi na Nigeria sune zasu kasance manyan jagororin tattaunawan ta bangaren gwamnatin tarayya.

Duk a yau din kuma, gwamnatin tarayya zata kara yin wani zama tare da ministan ilimi da kuma shugabannin kungiyar malaman jami'oin ƙasar nan domin ganin an kawo karshen yajin aikin da suka tsunduma kusan watanni biyu kenan, ana fatan kawo karshen wannan yajin aikin a yau.

Comments

Popular posts from this blog

Zan Kawo Karshen Kashe-Kashen Zamfara Cikin Wata Daya - ATIKU ABUBAKAR

Dan Sanda Ya Kashe Matasa Biyu A Benin

Minista Sanye Da Kayan Ala'ada