Taron Mjalisar Dinkin Duniya 68th
 
    A jiya talata ne majalisar dinkin duniya ta bude taronta wanda tasaba yi duk shekara-shekara karo na 68 th  a babban ginin majalisar dake birnin New York na kasar America   Taron yazo ne dai-dai lokacin da kasashen yamma suke nuna ma kasar Syria yatsa akan zargin da akeyma gwamnatin kasar na amfani da makamai masu guba a yakin basasan da ya kusa kwashe sekaru 3 ana gwabaza da ‘yan tawayen kasar .   Akuma   dai dai lokacinda ake ci gaba d a cacar baki tsakanin Amurka  da Rasha, kan wanda  za'a azawa alhakin kai hari da makamai masu guba a Syria . Hakanan kuma an fara ganin alamun Iran ta fara sassautowa daga tafarkin fito na fito da manyan kasashen duniya kan shirin nukiliyar  d a ake zargin tana fakewa da  shi ne domin habaka makaman nukiliya.   Haka kuma akwai batun yaki da ta’addance da kasahsen duniya suke ikararin sunayi a duniyar, inda wannan zaman yazo dai-dai da lokacin da kungiyar  Al-Shabab  ta kaddamar da wani hari a birnin nairobi na Kenya.   Haka kuma...